Hausa

Surah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) - Aya count 182
Share
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.