Hausa

Surah Ash-Shuara ( The Poets ) - Aya count 227
Share
¦. S̃. M̃.
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?